An Sami Nasarar Gano Wacce Ta Kama Salla Lokacin Da Take Talla

Posted by

An Sami Nasarar Gano Wacce Ta Kama Salla Lokacin Da Take Talla

Idan baku manta ba a kwanakin baya Jaridar Amintacciya ta rawaito muku cewa, wani mai anfani da kafafen Sada Zumunta Abdulmudallib Hamza Kibiya ne ya hangi wannan baiwar Allah tana Sallah dai dai lokacin da take yawon talla, ganin haka yasa ya dora a shafin sa na Facebook.

Sakamakon haka ne yasa labarin matashiyar ya zagaye kafafen Sada Zumunta inda jama’a da dama ke neman yadda za’a gano inda take.

Cikin ikon Allah kamar yadda ya bayyana, a yau ne ya sami haɗuwa da wannan baiwar Allahn wacce tai Sallah a kasuwa Bayan kwashe kwanaki 6 ana Nemanta.

Kamar yadda ya bayyana yanzu haka zai tafi da ita gidansu, domin suyi Magana da iyayenta.

Wane fata za kuyi mata ?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *