Yanzun Kimanin Shekaru 9 Kenan Da Rasuwar Marigayi Fadar Bege Allah Ubangiji Yayi Mashi Rahama Amin

Posted by

Yanzun Kimanin Shekaru 9 Kenan Da Rasuwar Marigayi Fadar Bege Allah Ubangiji Yayi Mashi Rahama Amin

YAU SHEKARU 9 DA RASUWAR MARIGAYI UMAR ABDULAZIZ BABA FADAR BEGE.

An haifi Umar Abdul-Aziz Baba da akafi sani da (Fadar Bege) a garin Garko karamar Hukumar Wudil a Ta Wancan Lokacin, wanda a yanzu tazama Karamar Hukuma mai zaman kanta a Jihar Kano, a ranar Alhamis a shekarar 1974.

Mahaifinsa Mal Umar, mai Unguwa ne a wani kauye dake garin Garko, bayan rasuwar mahaifin Fadar Bege lokacin yana dan shekar hudu (4) sai suka dawo Karamar Hukumar Wudil da zama shida mahaifiyarsa mai suna Malama Hadiza, kasancewar dama aikine yakai mahaifin nasa na Mai Unguwa garin na Garko lokaci da take hade da karamar hukumar Wudil.

FARA KARATUN ALQURANIN SA.

Fadar Bege ya fara karatun Alonsa ne a wata makaranta mai suna MAKARANTAR MALAM YAYA, a wurin wani mashahurin Malami dake cikin Karamat Hukumar Wudil mai suna Alaramma Malam Musa Yaya, wanda a yanzu haka shine shugaban Malamai na Karamar Hukumar Wudil.

FARA KARATUN BOKONSA.

Fadar Bege ya fara Karatunsa na Primary a Wudil Special Primary School a shekarar 1981, ya kamala karatunsa na Primary a shekarar 1986.

Sanan ya tafi Makarantar Koyan Kasuwanci dake Wudil, wato Government Secondary Commercial School Wudil a shekarar alif 1986, ya kuma kammala karatun a shekarar alif 1992.

Fadar bege bai tsaya a nan ba bayan kammala karatunsa na Sakandire, sai kuma ya famtsama akan neman karatun adini iri daban daban a gurin Maluma masu tarin yawa, na ciki da wajen garin wudil, a karshe yazama shima mai bada karatu a Islamiya dake garin na wudil

SANA’O’IN DA YAYI.

Marigayi Fadar Bege yayi sana’o’i da dama daga ciki har da wacce akasan duk wani dan wudil da yinta wato sana’ar dinkin Kwado Da Linzami.

Sannan marigayi Fadar Bege yayi sanar Tireda bai tsaya a iya nan ba yayi sanar daukar hoto.

Sanan yana hadin gwiwa da mahaifiyarsa wajen sana’ar Shinkafa.

Marigayi Fadar Bege yafara buga Mandiri ne a wata Kungiya mai suna Fitiyano.

Kasancewar basirar da Allah yabawa marigayi fada a harkar sai abokai suka fara bashi shawarar cewa ya fara

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *